Kamfanin Dillancin Labaran ƙasa da ƙasa na Ahlul-Bayt (AS) – ABNA – ya ruwaito cewa: Sheikh Sunusi Abdulkadir, Wakilin mabiya harkar Musulunci a birnin Kano na Najeriya, a cikin wani jawabi a Masallacin Fagge, ya yi nazari kan halin da duniya ke ciki a yanzu, yanayin musulmi da nauyin da ya rataya a wuyan mabiya makarantar muslunci game da abubuwan da ke faruwa a wannan zamanin.
Ya yi jawabi ga musulmi musamman ɗalibai da mabiya Sheikh Ibrahim Zakzaky (Allah ya kiyaye shi), yana mai bayyana cewa yau, lokacin fata ne, girma da kuma jiran nasara, kuma waɗanda ke tunanin tabbatar da addinin Allah da ikinsa, ya kamata su taka rawar gani da dukkan ƙarfinsu kan hanyar gaskiya da hadafin musulunci.
Sheikh Sunusi Abdulkadir ya kuma yi Ishara dangane da iƙirarin ƙarfin Amurka da gwamnatin Sahayoniya, yana mai nanata cewa: yaɗa farfagandar ƙarfin Amurka da gwamnatin Sahayoniya da fifikonsu, ba zai iya ɓoye gaskiyar da ke akwai ba kuma yawancin gaskiya da raunin da suke da shi sun bayyana ga duniya.
Ya yi nuni da cewa: abubuwan da ke faruwa a duniya suna nuni da cewa yanayi ba ya tsayawa a waje ɗaya koyaushe kuma kowane lokaci yana da yanayinsa da buƙatunsa na musamman; don haka, muminai ya kamata bisa dogaro da ilimi da sani, haƙuri da tsayin daka su gudanar da nauyin da ya rataya a wuyansu a lokacin da ya dace.
Bayan kammala jawabin wannan malamin addini, waɗanda suka halarta a taron sun karanta addu'o'i na musamman don nasarar Jamhuriyar musulunci ta Iran da al'ummar Yemen kuma sun nuna goyon baya da godiya ga gwagwarmaya da juriyar al'ummar wannan ƙasa kan Amurka da Saudi Arabiya.
A ci gaba da wannan taron, an yi addu'a ga Allama Sheikh Ibrahim Zakzaky (Allah ya kiyaye shi) da dukkan mabiya harkar musulunci kuma waɗanda suka halarta sun roƙi Allah Maɗaukaki nasara da ɗaukaka gare su.
An gudanar da wannan taro ne a cikin tsarin tunatarwa da shirye-shiryen ranar Juma'a a Masallacin Fagge na birnin Kano.
……….
Ra'ayinka